Chapter 96 (Sura 96)
1; Ka yi karatu da sunan Ubangijinka, wanda Ya yi halitta.
2; Ya hahitta mutum daga gudan jini.
3; Ka yi karatu, kuma UbangiJinka shi ne Mafi karimci.
4; Wanda Ya sanar (da mutum) game da alƙalami.
5; Ya sanar da mutum abin da bai sani ba.
6; A´aha! Lalle, ne mutum haƙĩƙa, yana girman kai (ya ƙi karatu).
7; Dõmin yã ga kansa, yã wadãta.
8; Lalle ne zuwa ga Ubangijinka makoma take.
9; Shin, kã ga wanda ke hana.
10; Bãwã idan yã yi salla?
11; Ashe, kã gani, idan (shi bãwan) ya kasance a kan shiriya?
12; Ko ya yi umurni da taƙawa?
13; Ashe, kã gani, idan (shi mai hanin) ya ƙaryata, kuma ya jũya bãya?
14; Ashe, bai sani ba cewa Allah Yanã gani?
15; A´aha! Lalle ne, idan bai hanu ba, lalle ne zã Mu ja gãshin makwarkwaɗa.
16; Makwarkwaɗa maƙaryaciya, mai laifi.
17; Sai ya kirayi ƙungiyarsa.
18; Zã Mu kirayi zabaniyãwa (mala´iku mãsu girma).
19; A´aha kada ka bĩ shi. Kuma ka yi tawali´u,(5) kuma ka nemi kusanta (zuwa ga Ubangijinka).
Hausa Quran | Karanta Al-Qur’ani
Pages: 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114