Chapter 82 (Sura 82)
1; Idan sama ta tsãge.
2; Kuma idan taurãri suka wãtse.
3; Kuma idan tħkuna aka facce su.
4; Kuma idan kaburbura aka tõne su.
5; Rai yã san abin da ya gabatar, da abin da yã jinkirtar.
6; Yã kai mutum! Mħ ya rũɗe ka game da Ubangijinka, Mai karimci.
7; Wanda Ya halitta ka sa´an nan ya daidaitã ka, Ya kuma tsakaitã ka.
8; A cikin kõwace irin sũra Ya so Ya ginã ka a kanta.
9; A´aha, bã haka ba, kuna ƙaryatãwa game da sakamako!
10; Lalle ne, a kanku, haƙiƙa akwai matsara.
11; Mãsu daraja, marubũta.
12; Sunã sanin abin da kuke aikatãwa.
13; Lalle ne, mãsu ɗã´ã ga Allah, dãhir, suna cikin ni´ima.
14; Kuma lalle ne, fãjirai, dãhir, sunã cikin Jahĩm.
15; Zã su shigħ ta a rãnar sakamako.
16; Bã zã su faku daga gare ta ba.
17; Kuma mħ ya sanar da kai abin da ake cħ wa rħnar sakamako?
18; Sa´an nan, mħ ya sanar da kai abin da ake cħ wa rãnar sakamako?
19; Rãnã ce da wani rai ba ya iya mallakar kõme dõmin wani rai al´amari, a rãnar nan, ga Allah (ɗai) yake.
Hausa Quran | Karanta Al-Qur’ani
Pages: 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114